• Tue. Jun 17th, 2025

Global Tracker

Truth and Objectivity

Rasha Ta Karɓi Shugabancin Kwamitin Tsaro Na MDD

ByGlobal Tracker

Apr 1, 2023

Kasar Rasha ta karɓi shugabancin kwamitin taro na Majalisar Ɗinkin Duniya duk da ƙoƙarin makociyar Rashan wacce kuma suke yakar juna a yanzu wato Ukraine na ganin hakan bai tabbata ba.

Duka mambobin kwamitin 15 sukan jagoranci kwamitin tsawon wata guda a wani tsarin shugabancin kwamitin na karɓa-karɓa.

Rabon da Rasha ta jagoranci kwamitin tun a watan Fabrairun 2022, lokacin da ta ƙaddamar da ta fara yaki da kasar Ukraine.

Hakan na nufin a yanzu kwamitin tsaron na Majalisar Dinkin Duniya na ƙarƙashin jagorancin ƙasar da shugabanta ke fuskantar yiwuwar kamu kan zargin laifukan da suka shafi yaƙi.

KU KARANTA: Rasha ta Kama Dan Jaridar Amurka Bisa Zargin Leken Asiri

A watan jiya ne kotun hukunta manyan laifuka ta duniya wadda ba a ƙarƙashin Majalisar Dinkin Duniya take ba – ta ba da sammacin kama shugaban Rasha Vladimir Putin.

Duk da ƙorafin da Ukraine ta yi, Amurka ta ce ba za ta iya hana Rasha – wadda ke da kujerar dindindin a kwamitin tsaron – ɗarewa kan shugabancinsa ba.

Sauran ƙasashen da suke da kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya sun haɗar da Birtaniya da Amurka da Faransa da kuma China.

 

BBC Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *