Customize Consent Preferences

We use cookies to help you navigate efficiently and perform certain functions. You will find detailed information about all cookies under each consent category below.

The cookies that are categorized as "Necessary" are stored on your browser as they are essential for enabling the basic functionalities of the site. ... 

Always Active

Necessary cookies are required to enable the basic features of this site, such as providing secure log-in or adjusting your consent preferences. These cookies do not store any personally identifiable data.

No cookies to display.

Functional cookies help perform certain functionalities like sharing the content of the website on social media platforms, collecting feedback, and other third-party features.

No cookies to display.

Analytical cookies are used to understand how visitors interact with the website. These cookies help provide information on metrics such as the number of visitors, bounce rate, traffic source, etc.

No cookies to display.

Performance cookies are used to understand and analyze the key performance indexes of the website which helps in delivering a better user experience for the visitors.

No cookies to display.

Advertisement cookies are used to provide visitors with customized advertisements based on the pages you visited previously and to analyze the effectiveness of the ad campaigns.

No cookies to display.

  • Wed. Jul 16th, 2025 7:12:33 PM

Global Tracker

Truth and Objectivity

Muna Bawa Inganta Rayuwar Marayu Fifiko a Koda Yaushe — Sani Wakili

ByGlobal Tracker

Apr 10, 2023

DAGA: IBRAHIM AMINU RIMIN-KEBE

 

Zababban dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Minjibir da ungogo, a jam’iyyar NNPP, Honarabil Sani Adamu Wakili ya jagoranci rabon kayan sallah ga marayu kimanin 320 a kananan hukumomin Minjibir da ungogo a jihar Kano.

Dan majalisar ya bayyana cewa, koda a shekarar data gabata sun dinkawa marayu kimanin 150 kaya tare da basu kyauta domin gudanar da bikin sallah kamar kowa.

Wakili, yana mai bayyana cewa, akwai bukatar wadata dake cikin al’umma dasu tashi tsaye wajen cigaba da tallafawa rayuwar marayu da kuma marasa karfi dake kusa dasu a wannan lokacin na matsin tattalin arziki.

A ranar asabar din data gabata ne Honarabil Sani Adamu Wakili ya jagoranci rabon kayan sallah ga marayun a karamar hukumar Minjibir wacce take da mazabu 11 wanda ya gudana a cikin garin minjibir taron daya samu halartar zababban dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar minjibir Honarabil A.A Minjibir.

KU KARANTA: VIDEO: Yadda Shugaban Kamfanin “Dan-kata Investment” Ya Rabawa Mutane Kusan 2,000 Kayan Abinci

Hakazalika a ranar lahadin data gabata rana ta karshe, Honarabil Wakili jagoranci rabon kayan sallah ga marayun a karamar hukumar ungogo mai mazabu 11 wanda ya gudana a cikin garin ungogo wanda Kuma ya samu halartar dan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar ungogo a majalisar dokokin jihar Kano Honarabil Aminu Sa’adu Ungogo, Shugaban jam’iyyar NNPP na karamar hukumar ungogo Alhaji Bilyaminu Bachirawa da sauran manyan baki.

Lokacin da marayun ke karbar Tallafin.

Dan majalisar tarayya, ya tabbatar da cewa zai mai mayar da hankali a fanin harkokin kiwon lafiya dakuma ilimi a kananan hukumomin guda biyu.

Ya Kara da cewa, akwai batun samarwa da matasa aiyukan wadanda zasu dogara da kan su dakuma baiwa mata jarin dasu dogara da kan su dan kaucewa zaman kashe wando.

Daga bisani zababban dan majalisar tarayyar, ya tabbatar da cewa zai bakin kokarin sa da zarar ya kama aiki domin samar da abubuwan more rayuwa ga al’ummar da yake wakilta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *