Akalla mutane 36 ne suka mutu a wasu tashe-tashen hankula a jihar Puntland da kuma yankin Lower Shabellebiyu da ke ƙasar Somalia.
Likitoci sun ce aƙalla mutane 26 ne suka mutu a wani kazamin fada da aka gwabza a ranar Talata a yankin Garoowe, babban birnin jihar Puntland.
Haka kuma wasu 10 suka mutu bayan wasu bama-bamai da aka sarrafa daga nesa suka tashi a wani ƙauye kudu maso yammacin Mogadishu babban birnin kasar ta Somalia.
KU KARANTA: Shugabannin Afrika na Shirin Sulhunta Rikicin Sudan
Shaidu sun ce mutane da dama ne suka mutu a fashewar bam na farko sannan bam na biyu ya tashi a lokacin da fararen hula da sojoji suka je wajen domin aikin ceto.
BBC Hausa