• Wed. Dec 10th, 2025

Global Tracker

Truth and Objectivity

Darikar Tijjaniyya Ta Yabawa Gwamnan Kano Bisa Nadin Barista Dan-almajiri Shugaban Hukumar Zaka

BySani Magaji Garko

Dec 13, 2024

DAGA: KAMAL YAKUBU ALI, KANO

Majalisar Shura ta darikar Tijjaniyya ta kasa a madadin daukacin mabiya darikar Tijjaniyya sun yabawa gwamna jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa nadin da ya yiwa Sakataren Majalisar Shura ta Darikar Tijjaniyya Barrista Imam Sheikh Habibu Muhammad Dan Almajiri a Matsayin shugaban Hukumar Zakka da Hubusi ta Jihar Kano.

Shugaban majalisar Khalifa Sheikh Sani Shehu Maihula a wata tattaunawarsa da wakilin GLOBAL TRACKER a Kano ranar Juma’a.

Ya ce hakika an ajiye kwarya a gurbinta, inda ya bayyana barrista Dan àlmajiri a matsayin jajirtacce wajen gudanar da ayukansa ba tare da nuna gazawa ba.

KU KARANTA: Gaskiya Ita ce Babbar Siffar Mumini — Barista Dan-almajiri

Shugaban ya kuma bukaci gwamnatin jihar Kano data bashi dukkan goyan bayan da ya dace domin ganin ya dawo da martaba hukumar, kasancewarsa gogagge wanda ya saba gudanarda da muamaloli da mutane daban daban a fannoni na rayuwa.

A karshe yayi addua ga barrista Dan-almajir ya kuma yi masa fatan sauke nauyin da aka dora masa da kuma neman taimakon ubangiji a yayin gudanarda ayyukansa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *