Customize Consent Preferences

We use cookies to help you navigate efficiently and perform certain functions. You will find detailed information about all cookies under each consent category below.

The cookies that are categorized as "Necessary" are stored on your browser as they are essential for enabling the basic functionalities of the site. ... 

Always Active

Necessary cookies are required to enable the basic features of this site, such as providing secure log-in or adjusting your consent preferences. These cookies do not store any personally identifiable data.

No cookies to display.

Functional cookies help perform certain functionalities like sharing the content of the website on social media platforms, collecting feedback, and other third-party features.

No cookies to display.

Analytical cookies are used to understand how visitors interact with the website. These cookies help provide information on metrics such as the number of visitors, bounce rate, traffic source, etc.

No cookies to display.

Performance cookies are used to understand and analyze the key performance indexes of the website which helps in delivering a better user experience for the visitors.

No cookies to display.

Advertisement cookies are used to provide visitors with customized advertisements based on the pages you visited previously and to analyze the effectiveness of the ad campaigns.

No cookies to display.

  • Tue. Jul 15th, 2025 2:00:13 PM

Global Tracker

Truth and Objectivity

Zamu Duba Yiwuwar Kara Alawus Din Limamai Da Ladanai — Shugaban K/H Dala

BySani Magaji Garko

Feb 4, 2025

DAGA: SANI MAI-WAYA RIJIYAR LEMO, KANO

Majalisar karamar hukumar Dala ta ce tana duba yiwuwar kara Alawus din Limamai da Ladanai a yankin domin jindadin cigaba da ilimintar da al’umma.

Shugaban karamar hukumar Alhaji Surajo Ibrahim Imam ne ya bayyana hakan a wani taro na musamman da limaman a sakatariyar karamar hukumar.

A lokacin taron, shugaban ya bayyana Limamai a matsayin kashin bayan cigaban al’umma.

KU KARANTA: Sanata Kawu Sumaila da Kwamishinan Yan Sandan Kano Sun Ziyarci Gurin Rikici Tsakanin Al’umma da Yan Sanda a Wudil

“Tun lokacin da na kama aiki a matsayin shugaban karamar hukumar Dala kungiyoyi daban-daban sun zo don tayani murna, amma banga kungiyar Limamai da Ladanai ba, wannan shine ya sa na gayyace ku domin naji daga bakin ku, mu ga yadda zamu inganta harkokin ku,” inji Surajo Imam.

Ya ce zasu tabbatar da bada gudun mowa don cigaban al’umma musamman masu ilimin addinin musulunci la’akari da yanayin tattalin arzikin da ake ciki.

Ya kuma bukace su da su cigaba da tabbatar da gwaji kafin daura Aure don gudun samun iyalai da basu da ingantacciyar lafiya.

A jawabinsa, shugaban Limaman masallatan juma’a na Dala Malam Nura Arzai ya yabawa shugaban karamar hukumar bisa gayyatar su da akayi inda ya ce sun dade sun jiran lokacin.

Malam Nura Arzai wanda kuma babban limaman masallacin juma’a na Mariya Sanusi Dantata dake kofar ruwa ya ce Dala tana da masallatan juma’a 34.

Ya bukaci gwamnatin yankin ta mayar da hankali kan gina Makarantun Al’qur’ani dana isilamiyya da kuma na koyan sana’o’i don cigaban al’umma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *