Matatar mai ta Dangote Ta sanar da sake rage kudin man Fetir a sannan Nigeriya ba ki daya.
Cikin wata sanarwa da kamfanin ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis ya ce ragin ya bambanta daga yanki zuwa wani yankin a fadin tarayyar Nigeriya.
Kamfanin ya ce za’a rika sayar da man kan naira 895 a jihar Kano da Arewa maso yamma da Arewa ta tsakiyar kasar nan.
Kamfanin ya ce za a riƙa sayar da litar mansa a Legos kan naira 875, yayin da za a riƙa sayar da litar a jihohin arewa maso yamma kan naira 895, sai kuma naira 905 a jihohin arewa maso gabashin Najeriya.