• Sat. Apr 11th, 2026

Global Tracker

Truth and Objectivity

Sarkin Musulmi Ya Sanar Da Ganin Watan Ramadan a Nigeriya

BySani Magaji Garko

Feb 17, 2026

Fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya, ta umarci Musulmi a fadin ƙasar nan su fara azumin Watan Ramadan a ranar Laraba 18 ga watan Fabrairun 2026.

Cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulumin ta fitar a ranar Talata da daddare ta ce an samu bayanan ganin watan a wurare daban-daban a ƙasar nan.

Matakin na alamta shigar watan Ramadan mai alfarma – wanda musulmi a faɗin duniya ke gudanar da ibadar azumi, ɗaya daga cikin shika-shikan musulunci biyar.

Don haka ne fadar ta sanar da Laraba 18 ga watan Fabrairu a matsayin ranar 1 ga watan Ramadan na 1447AH.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *