• Sun. Jul 20th, 2025

Global Tracker

Truth and Objectivity

Zargin Karya Dokar Hawan Sallah: Rundunar Yan Sandan Kano Ta Gayyaci Sarki Sanusi

BySani Magaji Garko

Apr 5, 2025

Rundunar yan sandan ta kasa ta gayyaci sarkin Kano Muhammadu Sanusi II bisa zargin karya dokar da ta saka na hana gudanar da hawan a lokutan bukukuwan karamar Sallah.

A cikin wasikar gayyatar mai lamba CR:3000/FID/FHQ/ABJ/VOL59/697 mai dauke da kwanan watan 2, Afirilun 2025, kwamishinan ƴan sanda Olajide Rufus Ibitoye ne ya sanya mata hanu a madadin matakin babban sifeton yan sanda mai kula da tattara bayanan sirri a rundunar yan sanda ta kasa dake Abuja ne.

“An umarceni na sanar da kai cewa babban sifeton yan sanda na kasa ta hanun mataimakinsa suna gayyatar ka a cigaba da gudanar da binciken da ake yi game da abinda ya faru a lokacin bukukuwan sallah a yankin ka,” inji takardar.

Ana sa ran sarkin na Kano zai halarci shalkwatar rundunar yan Sanda ta kasa dake Abuja da Karfe 10:00am a ranar Talata 8, Afirilun 2025.

KU KARANTA: Galadiman Kano Abbas Sanusi Ya Rasu

Sanarwar ta ce ana sa ran sarkin zai bada wasu bayanai ne wanda zasu taimaka a cigaba da binciken da rundunar ta ke yi.

Gayyatar sarkin na zuwa ne bayan rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar Kano ta kafa kwamitin mutane 8 domin gudanar da binciken kisan wani jami’in Vijilanti a ayarin sarkin a lokacin hawan Sallar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *