• Sat. Jul 12th, 2025

Global Tracker

Truth and Objectivity

YANZU-YANZU: Zulum Ya Samu Nasarar Komawa Wa’adi na Biyu

ByGlobal Tracker

Mar 20, 2023

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya sake samun nasarar komawa wa’adi na biyu na mulkin jihar, bayan nasarar da ya samu a zaɓen gwamna da aka gudanar a ransar Asabar ɗin da ta gabata.

INEC ce ta bayyana ɗan takara a matsayin wanda ya lashe zaɓen a Maiduguri babban birnin jihar a ranar Litinin.

KU KARANTA: APC Na Dab Da Lashe Zaben Gwamna a Jigawa

Zulum ya lashe zaɓen ne da ƙuri’a 545,542 sai kuma jam’iyyar PDP ta ke da ƙuri’u 82,147.

Jam’iyyar LP wadda ta taka rawar gani a zaɓen shugaban ƙasar Najeriya da aka yi a ranar 25 ga watan Fabirairu ta zo ta uku da kuri’a 1,517.

 

BBC Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *