• Wed. Dec 10th, 2025

Global Tracker

Truth and Objectivity

APC Ta Nemi INEC ta Soke Zabukan Cike Gurbi na Kano

BySani Magaji Garko

Aug 16, 2025

Jam’iyyar APC mai ta nemi hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa INEC ta dakatar tare da soke zaɓen cike gurbi da ke gudana yanzu haka a jihar Kano saboda “tashin hankali”.

Wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar ta ce ‘”‘yandaba sun tarwatsa kayayyakin zaɓe a ƙananan hukumomin Bagwai da Shanono da Gari”, inda ake gudanar da zaɓen ɗanmajalisar tarayya.

A cewarta: “Cigaba da kaɗa ƙuri’a a irin wannan yanayin na dabanci da tilasta wa masu zaɓe ya saɓa da tanadin dimokuraɗiyya na gudanar da sahihin zaɓe, kuma zai koyar da satar ƙuri’a da ba za a yarda da shi ba,” in ji sanarwar.

BBC Hausa ta rawaito cewa zuwa yanzu ba a kai ga samun sakamakon zaɓen a hukumance ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *