Mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya sanar da ganin jinjirin watan Ramadan.
Cikin wata sanarwa da Sarkin Musulmin, Sa’ad Abubakar lll ya karanta a fadarsa, ya ce an ga watan a sassan ƙasar daban-daban.
KU KARANTA: Sarkin Musulmi Ya Bada Umarnin Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan
Don haka ne ya ayyana ranar Asabar 1 ga watan Maris a matsayin 1 ga watan Ramadan 1446.
Tuni dai hukumomin Saudiyya suka sanar da ganin watan a ƙasar, inda suka ayyana gobe Asabar a matsayin ɗaya ga watan Ramadan a Saudiyya.